BBC

News

Sports

Business

Entertainment

GhanaWeb TV

Africa

Opinions

Country

Dalili 10 da Man City ta lashe Premier League na bana

Man City suka ci wasan firimiya

Sun, 21 May 2023 Source: BBC

Manchester City ta lashe Premier League na bana, bayan da Arsenal ta kasa cin Nottingham Forest ranar Asabar.

Nottingham ta yi nasara a City Ground da cin Gunners 1-0 a wasan mako na 37 a babbar gasar tamaula ta Ingila.

Arsenal wadda take da maki 81 da tazarar maki hudu tsakaninta da Manchester City ta dade tana dakon teburi daga baya aka karbe lokacin da wasannin suka zo karshe.

Hakan ne ya sa BBC ta yi duba ta zakulo dalili 10 da ta kai Arsenal ta rasa Paremier League na kakar nan.

1. Kwallon farko da Erling Haaland ya ci wa Manchester City

Kwallon da Erling Haaland ya fara ci wa City a bugun fenariti ya yi.

An fara bude labulen kakar bana da karawar Community Shield, inda Erling Haaland ya yi ta dubi-dubin cin kwallo, yayin da Darwin Nunez ya ci zura a raga a karawar da Liverpool ta yi nasara cin 3-1.

Nan da nan aka fara surutai kan cewar Haaland ba zai kai labari ba, amma sai ya zura kwallo biyu a wasan farko a Premier League da West Ham.

Sai dai bai ci Bournemouth ba a karawa ta gaba ba, daga nan ya zura a raga a kowacce karawa bakawi da City ta yi a dukkan fafatawa, har da cin uku rigis sau biyu a jere.

2. Manchester City ta yaga barakar Manchester United

A wasan hamayya Manchester City ta doke Manchester United da cin 6-3 a farkon watan Oktoba.

Haaland ya ci uku a karawar, shima Phil Poden ya zura uku a ragar United.

Wasan ya faranta ran magoya bayan City, yayin da United ta buga fafatawar da kwarin gwiwar cewar za ta yi wani abin kirki, bayan cin Arsenal 3-1.

3. De Bruyne' ya ci Leicester City a bugun tazara

Kevin de Bruyne ya ci Leicester City kwallo mai kayatarwa a bugun tazara daga yadi na 25.

A karshen watan Oktoba, Haaland ya fara buga dukkanin wasannin Manchester City har ma ya zura kwallo 22 a raga, amma bai yi fafatawar City a gidan Leicester ba.

City na bukatar cin karawar domin ta koma ta daya a kan teburi, kafin Arsenal ta karbi bakuncin Nottingham Forest a Emirates.

Bayan da suka koma zagaye na biyu ne aka samu bugun tazara daga yadi na 25, kuma Kevin De Bruyne ya dauka ya buga ta kuma fada raga suka hada maki uku.

4. Haaland ya ci fenariti daf da za a tashi wasa

Bayan da Gunners ke jan ragamar teburi, City ta kwan da sanin kada take barar da maki idan har tana son kamo Arsenal.

Nan da nan Fulham ta tayar da hankalin City ta zura kwallo a raga ta yi kokarin taka mata burkin cin wasa tara a jere a Etihad a dukkan fafatawa.

Kafin nan minti uku da take leda Haaland ya ci fenariti, bayan da aka yi wa De Bruyne keta, inda Haaland ya dauki kwallon ya buga ya kuma ci.

City ta sha wahala a wasan, wadda tun a minti na 26 aka bai wa Joao Cancelo jan kati, amma Julian Alvarez ya kara na biyu tun kan hutu, hakan ya mayar da City kan teburi.

5. Mahrez ya ci Chelsea, bayan da ya shiga wasa daga baya

Bayan da aka kammala wasannin Premier a 2022, Arsenal tana ta daya a teburi, hakan ya kara nuna cewar akwai jan aiki a gaban City idan har tana son kare kofinta na bara.

Ranar 5 ga watan Janairu City ta ziyarci Chelsea, wadda ta kwan da sanin idan aka doke ta a Stamford Bridge, Gunners za ta bata tazarar maki takwas tsakani.

Haka aka fara gumurzun ba ci, kuma lokaci na ja, daga nan ne Pep Guardiola ya tashi Jack Grealish da Riyad Mahrez, wadanda ke zaman benci ya saka su a wasan.

Ai kuwa kwalliya ta biya kudin sabulo, domin 'yan wasan biyu sun taka rawar gani da ta kai Mahrez ya ci kwallo a wasan da aka tashi 1-0.

6. Man City ta doke Arsenal a Emirates

Ranar 15 ga watan Fabrairu aka gwada kwazon Arsenal ko za ta iya lashe Premier League na kakar nan, wadda kaka 19 rabonta da shi.

Wasa ne tsakanin Arsenal da Manchester City, idan Gunners ta ci za ta bai wa kungiyar Etihad tazarar maki uku, amma idan City ta yi nasara za ta koma ta daya a kan teburi a karon farko bayan Nuwamba.

Bukayo Saka ne ya farke kwallon da De Bruyne ya fara ci, sannan Grealish ya kara na biyu, wanda ke kan ganiya tun bayan kammala gasar kofin duniya a Qatar.

Erling Haaland ne ya zura na uku a raga, wadanda suka je Emirates.

A wasan ne 'yar manuniya ta nuwa Manchester City za ta iya lashe kofin, domin damar hakan na hannunta, bayan kwantan wasa.

7. Saliba ya ji rauni a Emirates a Europa League

William Saliba bai sake yi wa Arsenal wasa ba tun bayan da ya ji rauni a karawa da Sporting Lisbon ranar 16 ga watan Maris a gasar Europa League.

Idan ka tambayi 'yan Arsenal za su ce maka rashin Saliba a fafatawar da ta yi ya kawo mata koma baya, wasu ma za su ce maka rashin ne ya sa ta kasa cin Premier a kakar nan.

Matashin dan wasan Faransa katanga ne a bayan Gunners kowa ya shaida hakan, amma sai ya ji rauni a Emirates a Europa League a wasan da Sporting ta cire Gunners a ranar ta 16 ga watan Maris.

Haka kuma a ranar Gunners ta rasa mai tsaron baya, Takehiro Tomiyasu, wanda shima har yanzu bai warke ba.

Daga nan Arsenal ta yi karawa bakwai kwallo na shiga ragarta a Premier League, in banda wanda ta ci Newcastle United 2-0 ranar 7 ga watan Mayu, lokacin City ta karbe ragamar teburi,

8. Arsenal ta bari Liverpool ta farke kwallo biyun da ta fara zurawa a raga

Matasan Liverpool sun je gidan Liverpool ta fatan hada maki uku a Anfield a karon farko tun bayan 2012.

Cikin minti 28, Arsenal ta zura kwallo 2-0 a ragar Liverpool, wanda hakan za ta bai wa City tazarar maki takwas tsakani, amma ina kan a tashi Liverpool ta farke suka tashi 2-2.

Daga nan ne aka fuskanci kalubalen da 'yan wasan Arsenal ke ciki a kokarin lashe kofin bana a karon farko tun bayan 2003/04.

Ita kuwa City sai ta samu damar komai yana hannunta, duk da cewar Arsenal ta bata tazarar maki shida, amma tana da kwantan wasa, sannan Gunners za ta je Etihad.

9. Saka ya barar da fenaritin da ya buga a wasan West Ham

Ba wanda ya yi tunanin Gunners za ta barar da maki a sauran wasannin da ke gabanta, bayan yin 2-2 da Liverpool.

Gabriel Jesus da Martin Odegaard suka ci West Ham kwallaye 2-0, bayan minti 10, amma daga baya Said Benrahma ya farke a minti na 33 a bugun daga kai sai mai tsaron raga, sannan Jarrod Bowen ya farke a minti na 54.

Wasa na biyu a jere da Arsenal ta tashi 2-2 kenan a Premier, bayan wanda ta yi a gidan Liverpool.

Tun bayan da Gunners ke cin West Ham 2-1 ta samu bugun fenariri, inda Saka ya dauka ya buga, amma ya barar, minti uku tsakani ne West Ham ta farke.

10. Man City ta ci Arsenal ta kara rage tazarar da ke tsakaninsu a teburi

Arsenal ta je Etihad a matakin ta farko a teburi da tazarar maki biyar tsakaninta da City mai kwantan wasa biyu, idan ta ci City za ta bayar da tazarar maki takwas.

Minti bakwai da take leda Kevin De Bruyne ya ci Arsenal, sannan wasu uku suka kara shiga ragar Gunners wadda ta zare daya aka tashi 4-1.

Daga nan ne damar Arsenal ta cin kofin Premier ta kara yin kasa, har wasu masu sharhin wasannin suka ci damar Gunners ta koma kaso 10 cikin 100.

To sai wasan da Brighton ta je har Emirates ta ci Arsenal 3-0 ya kara sa kungiyar ta yi ban kwana da babban kofin tamaula na Ingila a kakar nan.

A lokacin Arsenal tana da maki 81 ta biyu a teburi, City tana da maki 85, saura wasa uku a gabanta Arsenal kuwa biyu suka rage.

A wasan mako na 37 ne Arsenal ta ziyarci Nottingham Forest, wadda ke neman maki uku da zai tabbatar da ita a Premier League a kakar badi.

Ai kuwa sai Forest ta ci Arsenal 1-0, tun daga nan City ta zama ta lashe kofin bana na uku a jere kuma na biyar daga kaka shida.

Ranar Lahadi, City za ta kece raini da Chelsea a Etihad, sannan ta buga da Brighton ta kuma karkare da Brentford.

Source: BBC