Shugaban kungiyar kwallon kafa ta Tottenham Hotspur, Daniel Levy ya ce zai iya sayar da hannun jarinsa a kungiyar idan yin hakan yana da fa'ida ga kulob din.
Levy ne ke tafiyar da harkokin kulob din a madadin kamfanin ENIC wanda ya mallaki kashi 86.5%, yana kuma rike da mukamin shugaba tun 2001.
Magoya bayan kungiyar kwallon kafar sun yi kira ga Levy da ya ajiye mukaminsa sakamakon rashin kokarin da aka yi a kakar wasan da ta gabata.
Hankali ya dan kwanta a Tottenham a kakar wasar bana bayan nadin Ange Postecoglou a bazara, amma batutuwan da ke tasowa a wajen filin wasa sun sa an ci gaba da hura wa Levy wuta.
Dan kasuwan mai shekaru 61, ya tabbatar da cewa a baya bangarori da dama sun nuna sha’awarsu na mallakar kungiyar, musamman tun bayan da suka koma sabon filin wasa mai daukar yawan mutane 62,850 a shekarar 2019.
Ya bayyana cewa idan wani ya gabatar da tayi mai mahimmanci ga Tottenham, za a iya tattaunawa.
Kuma idan aka ga yana da muradin kulob din komai na iya faruwa.