BBC

News

Sports

Business

Entertainment

GhanaWeb TV

Africa

Opinions

Country

Duk wanda ya kwarmata masu ɓoye sabbin kuɗaɗe zai samu tukuici – EFCC

77812885 Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC

Mon, 13 Feb 2023 Source: BBC

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC a Najeriya ta ce bankunan kasuwanci ne suka janyo tarnaƙi wajen ganin sabbin kuɗi sun wadata a hannun jama'a.

EFCC ta ce bayanai daga Babban Bankin Najeriya sun nuna cewa zuwa yanzu, CBN ya buga sabbin takardun kuɗi sama da naira biliyan 400, amma bankuna sun ƙi fitarwa su bai wa jama'ar ƙasar.

Shugaban hukumar EFCC, Abdurrasheed Bawa a wata tattaunawa da BBC, ya buƙaci 'yan Najeriya su tona asirin masu ɓoye sabbin kuɗi, don ganin hukumar ta je ta ƙwace su.

Abdurrashe Bawa ya ce wannan ita ce mataki na gaba da suke ganin zai taimaka wajen kawo wa talakan Najeriya waraka.

Sannan ya tunasar da cewa akwai tukuici mai gwabi ga duk mutumin da ya taimaka aka gano wurare ko mutumin da ke rike da sabbin kudade.

'Ma’aikatan banki ne matsalar mu’

Shugaban na EFCC ya ce babu shaka sun yi na'am da wannan sauyi kuɗi, saboda bayanan sirri ya nuna musu cewa akwai mutane da dama da suka boye kuɗaɗe, suna cinikayya a boye.

Sai dai ya ce babbar matsalarsu ita ce ma'aikatan banki, saboda duk da cewa kuɗaɗen da aka buga ba su wadatu ba, ma'aikatan na bai wa wasu mutane kuɗaɗen a ɓoye.

"Su na hana talakawa kudaden a banki da na’urar ATM".

"Shiyasa mu ka tura jami'ansu jihohi domin sa ido kan bankunan da mutanen da ke yiwa harkar zangon kasa".

Zargin bai wa gwamnoni kuɗaɗe

Ya ce akwai zargin dagaske ana bai wa gwamnoni sabbin kuɗaden, kuma akwai wadanda suka boye tsoffi kuɗaɗe, shiyasa aka ba wa 'yan Najeriya damar kwarmata duk wani mutum da suka fuskaci na ɓoye kuɗaɗe.

EFCC ta tunasar da cewa duk mutum da ya tona asiri zai samu kasonsa mai gwaɓi, don haka kada mutane su yi kasa a gwiwa.

Source: BBC