BBC

News

Sports

Business

Entertainment

GhanaWeb TV

Africa

Opinions

Country

FA Cup: Tierney ne zai busa wasan Man United da Man City

Paul Tierney ne zai busa wasan hamayya tsakanin Manchester United da Manchester City

Fri, 19 May 2023 Source: BBC

Hukumar kwallon kafa ta Ingila ta babbatar da wadanda zai busa wasan karshe a FA Cup tsakanin kungiyoyin Manchester a watan Yuni.

Paul Tierney ne zai busa wasan hamayya tsakanin Manchester United da Manchester City da za su kara a Wembley ranar 3 ga watan Yuni.

Tierney shine zai ja ragamar mutum bakwai da za su yi alkalancin karawar farko da kungiyoyin za su yi a wasan karshe a FA Cup.

City ta kwao wannan matakin bayan da ta ci Sheffield United 3-0 a wasan daf da karshe ranar 22 ga watan Afirilu.

United kuwa doke Brigton 7-6 ta yi a nugun fenariti, bayan da suka tashi 0-0 ranar 23 ga watan Afirilu.

United tana da FA 12, ita kuwa City tana da shida, bayan da Arsenal ce kan gaba a yawan lashe kofin mai 14 jimilla.

Alkalin, wanda ya busa wa United karawa hudu a bana, yana da kwarewa a alkalancin wasan karshe a FA Cup, wanda ya yi mataimaki a 2010 a wasan Chelsea da Portsmouth.

Wadanda za su rike labule sun hada da Neil Davies da Scott Ledger da mai jiran ko-ta-kwana, yayin da Peter Bankes ne alkali na hudu.

David Coote ne zai kula da VAR, yayin da Simon Long zai taimaka masa.

Alkalan da za su busa wasan karshe a FA Cup na 2023

Alkali: Paul Tierney

Mataimaka: Neil Davies da Scott Ledger

Alkali na hudu: Peter Bankes

Mai jiran ko-ta-kwana: Adrian Holmes

Mai kula da VAR: David Coote

Mataimakin mai kula da VAR: Simon Long

Source: BBC