Menu

Gasar kofin duniya ta mata: Fifa ta yi barazana ga wasu kasashen Turai

Hoton alama

Tue, 2 May 2023 Source: BBC

Shugaban hukumar Fifa, Gianni Infantino ya yi barazanar kin nuna gasar kofin duniya ta mata ga wasu kasashen Turai biyar.

Infantino ya bukaci kasashen da cewar sai idan kamfanonin da za su haska gasar a talabijin sun kara kudin tayin da suka yi tun farko.

Shugaban ya ce abin da takaici kan kudin da aka yi tayin tallata wasannin a Burtaniya da Sifaniya da Italiya da Jamus da kuma Faransa.

Ya kara da cewar an watsa wa 'yan wasa da kwallon kafar mata kasa a ido, kuma manyan kasashen Turai na shirin kawo koma baya a gasar.

Za a buga gasar kofin duniya ta mata a Australia da New Zealand da za a fara ranar 20 ga watan Yulin 2023.

Infantino ya ce kamfanonin Turai da za su tallata gasar sun yi tayin biyan dalar Amurka miliyan daya zuwa miliyan 10 idan ka kwatanta da dalar Amurka miliyan 100 zuwa miliyan 200 wajen tallata gasar kofin duniya ta maza.

Ya ce wannan tayin ba adalci, idan suka dage iya abin da za su biya kenan, hakan zai hana Fifa ta bayar da izinin nuna gasar a kasashen.

Infantino ya kara da cewar dukkan kudin da za a samu a kallon gasar ta bana za a zuba su a fannin bunkasa kwallon kafar mata a duniya.

Infantino ya ce Fifa ta kara kudin ladan lashe kofin har linki uku zuwa dalar Amurka miliyan 152, idan aka kwatanta da abin da ta biya gasar a 2019 a Faransa.

Haka kuma Fifa na fatan biyan ladan cin kofin duniya na mata ya zama bai daya da yadda ake bai wa maza daga nan zuwa 2026/27 kamar yadda aka amince a taron da ta gudanar a cikin watan Maris.

Kamar yadda Fifa ta sanar kimanin mutum biliyan 1.12 ne suka kalli gasar kofin duniya ta mata a Faransa a 2019.

Ita ce gasar da mutane da yawa suka kalli kwallon kafar mata a tarihi.

Source: BBC