BBC

News

Sports

Business

Entertainment

GhanaWeb TV

Africa

Opinions

Country

Ina neman afuwan Musulmai kan kalamaina – Kashim Shettima

64083115 Maitamakin shugaban Najeriya Sanata Kashim Shettima

Sun, 18 Jun 2023 Source: BBC

Maitamakin shugaban Najeriya Sanata Kashim Shettima ya ce yana neman afuwan al'ummar Musulmi bisa wadansu kalamai da ya yi kan zaɓen shugabannin majalisar dokokin Najeriya.

A cewarsa ba a fahimci maganar a sigarta ba, kuma ba shi da wata manufa na ɓata sunan addininsa.

Sanata Kashim a tattaunawarsa da BBC ya ce ya yi waɗannnan maganganu ne saboda maslahar Najeriya, ganin cewa suna da wasu bayanai na sirri da bai dace ya fito yana faɗi ba.

Sannan yadda lamura ke tafiya a Najeriya a wannan lokaci, dole shugabanni su fito su ja hankali domin wanzuwar kasar baki-ɗaya.

Kalaman Shettima a cikin makon da ya gabata ya haifar da zazzafar muhawara musamman a shafukan sada zumunta inda aka rinƙa sukar mataimakin shugaban kasar.

Sai dai Kashim Shettima ya ce shi Musulmi ne na haƙiƙa domin zuri'arsu sun shafe tsawon dubban shekaru kan tafarkin addinin Islama.

Sannan duk wanda bai jidadin kalamansa ba, ya yi hakuri a yafe masa, ba shi da niyyar cutar da addini.

"Ni ɗan adam ne kuma ajizi don haka ina neman afuwan al'umma da Ubagijina".

Kashim Shettima ya tunasar da cewa shi ɗan malamai ne kuma jikan malamai, don haka ba shi da niyyar muzantawa wani ɓangare na addinin kasar.

Source: BBC