BBC

News

Sports

Business

Entertainment

GhanaWeb TV

Africa

Opinions

Country

Kotun daukaka ƙara ta kori ƙarar Nnamdi Kanu

90762908 Mazi Nnamdi Kanu

Thu, 13 Oct 2022 Source: BBC

Kotun daukaka ƙara ta Najeriya ta kori ƙarar gwamnati tarayya a kan jagoran ƙungiyar ƴan aware ta IPOB Nnamdi Kanu, ta hanyar yin watsi da dukkan tuhume-tuhumen da ake yi masa. Tawagar alkalan ta mutum uku da Mai Shari'a Jummai Hanatu ta jagoranta ta ce Kanu ba shi da laifin amsawa saboda tun farko Babbar Kotu ba ta da hurumin yi masa shari'a tun farko. Hukuncin kotun ya ce matakin kamo Kanu da aka yi da dawo da shi Najeriya daga Kenya ya kauce wa doka. Alkalan sun ce an dawo da shi Najeriya ne ba bisa ƙa'ida ba. Sannan sun ce gwamnatin tarayya ta gaza faɗar wajen da ta kama Kanu duk da manya-manyan zarge-zargen da take yi masa. Kotu ta ƙara da cewa shirun da gwamnatin ta yi na nuna cewa ta yarda da abin da Kanu ya ce cewa sato shi aka yi aka dawo da shi Najeriya da ƙarfi. Kotun ta ce tsare Kanu da yi masa shari'a a kowace kotu karya doka ne tun da ba bisa ƙa'ida aka mayar da shi Najeriya ba.

Kotun daukaka ƙara ta Najeriya ta kori ƙarar gwamnati tarayya a kan jagoran ƙungiyar ƴan aware ta IPOB Nnamdi Kanu, ta hanyar yin watsi da dukkan tuhume-tuhumen da ake yi masa. Tawagar alkalan ta mutum uku da Mai Shari'a Jummai Hanatu ta jagoranta ta ce Kanu ba shi da laifin amsawa saboda tun farko Babbar Kotu ba ta da hurumin yi masa shari'a tun farko. Hukuncin kotun ya ce matakin kamo Kanu da aka yi da dawo da shi Najeriya daga Kenya ya kauce wa doka. Alkalan sun ce an dawo da shi Najeriya ne ba bisa ƙa'ida ba. Sannan sun ce gwamnatin tarayya ta gaza faɗar wajen da ta kama Kanu duk da manya-manyan zarge-zargen da take yi masa. Kotu ta ƙara da cewa shirun da gwamnatin ta yi na nuna cewa ta yarda da abin da Kanu ya ce cewa sato shi aka yi aka dawo da shi Najeriya da ƙarfi. Kotun ta ce tsare Kanu da yi masa shari'a a kowace kotu karya doka ne tun da ba bisa ƙa'ida aka mayar da shi Najeriya ba.

Source: BBC