Menu

Kante ya siya kulob a Belgium

N'Golo Kante

Fri, 30 Jun 2023 Source: BBC

N'Golo Kante ya sayi kungiyar Royal Excelsior Virton da ke mataki na uku a gasar kwallon Belgium.

Dan kwallon Faransa mai shekaru 32, zai maye gurbin Flavio Becca a matsayin shugaban kulob din daga ranar 1 ga watan Yuli.

Kante ya bar Chelsea inda ya kulla yarjejeniya da kungiyar Al-Ittihad ta Saudiyya.

"Flavio na cikin matukar jin dadin da zai mika raganar kulob din ga N'Golo Kante," in ji wata sanarwa.

Kungiyar na kokarin komawa matakin farko a gasar kwallon Belgium.

Kante ya soma murza leda ne a karamar kungiyar Boulogne a Faransa kafin ya koma Caen a shekara ta 2013.

Ya taimakawa Leicester City lashe gasar Premier a 2016 kafin ya koma Chelsea inda ya lashe gasar zakarun Turai da kuma na Premier da kuma kofin FA.

Source: BBC