BBC

News

Sports

Business

Entertainment

GhanaWeb TV

Africa

Opinions

Country

Kotu ta fara zaman bayyana hukuncin zaɓen shugaban Najeriya

Supreme Court Of Nigeria Nigeria Supreme Court will be the final arbiter of petioners want to go further

Wed, 6 Sep 2023 Source: BBC

Kotun sauraron ƙararrakin zaɓen shugaban ƙasa a Najeriya, ta fara zama don gabatar da hukunci a kan ƙorafe-ƙorafen da wasu 'yan takara suka shigar mata, bayan zaɓen watan Fabrairun 2023.

Jami'an tsaron da aka jibge tun da sanyin safiya, sun datse titin da ke zuwa harabar kotun ɗaukaka ƙara ta Najeriya, inda ake zaman.

Kotun mai alƙali biyar a Abuja ta shafe watanni tana karɓar bahasi da kuma sauraron muhawara game da ƙorafe-ƙorafen maguɗi da jam'iyyun adawa na PDP da LP suka yi.

Tsohon gwamnan jihar Legas, Bola Ahmed Tinubu ne ya lashe zaɓen Najeriya, inda ya samu yawan ƙuri'un da suka kai kashi 37 cikin 100 a zaɓen ranar 25 watan Fabrairu. Abin da ya ba shi galaba a kan Atiku Abubakar na PDP da kuma Peter Obi na jam'iyyar LP.

Wannan, ba shi ne hukuncin ƙarshe da mai yiwuwa za a iya samu game da zaɓen ba, masana shari'a na cewa jam'iyyu na iya ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Ƙoli wadda za ta yanke hukunci na ƙarshe.

An ga manyan jami'an gwamnatin Najeriya ciki har da mataimakin shugaban ƙasar, Kashim Shettima da shugaban jam'iyyar APC, Abdullahi Umar Ganduje da gwamnonin jam'iyyar, duk sun hallara a kotun.

Haka zalika, akwai wasu gwamnonin adawa kamar na jihar Bauchi, Bala Mohammed a kotun da shugaban PDP, Umar Iliya Damagum.

Mai shari'a Haruna Tsammani tare da sauran alƙalan kotun sun fito inda suka zauna don fara gabatar da hukunci.

Source: BBC