Kylian Mbappe na jin cewar Paris St Germain ta ''yaudare shi'' yana son barin kungiyar a watan Janairu in ji Julien Laurens mai sharhin tamaula a Faransa. A watan Mayu dan kwallon tawagar Faransa ya saka hannu kan yarjejeniyar ci gaba da taka leda kaka uku a PSG, amma yanzu yana jin ya yi ''kuskure''. Mbappe, wanda ya ci kwallo 12 a dukkan wasan da ya yi wa PSG a bana na son komawa taka leda Real Madrid. Sai dai daraktan wasanni na PSG, Luis Campos ya ce dan kwallon mai shekara 23 bai taba cewar zai bar kungiyar a Janairu ba.
Kylian Mbappe na jin cewar Paris St Germain ta ''yaudare shi'' yana son barin kungiyar a watan Janairu in ji Julien Laurens mai sharhin tamaula a Faransa. A watan Mayu dan kwallon tawagar Faransa ya saka hannu kan yarjejeniyar ci gaba da taka leda kaka uku a PSG, amma yanzu yana jin ya yi ''kuskure''. Mbappe, wanda ya ci kwallo 12 a dukkan wasan da ya yi wa PSG a bana na son komawa taka leda Real Madrid. Sai dai daraktan wasanni na PSG, Luis Campos ya ce dan kwallon mai shekara 23 bai taba cewar zai bar kungiyar a Janairu ba.