Menu

Najeriya za ta kara da Afirka ta Kudu a wasan neman gurbin kofin duniya

Logon CAF

Fri, 14 Jul 2023 Source: BBC

Tawagar Super Eagles ta Najeriya za ta kara da Afirka ta Kudu da Benin da Rwanda da Zimbabwe da kuma Lesotho a wasan rukuni na uku na gasar cin kofin duniya da za a yi a shekara ta 2026.

A ranar Alhamis ne aka gudanar da bikin fitar da jadawalin gasan fitar da gwani a birnin Abidjan na ƙasar Ivory Coast.

Wasannin neman tikitin shiga gasar cin kofin duniya za a sake dawo da fafatawa tsakanin Najeriya da Afirka ta Kudu.

Sau 14 dai kasashen biyu sun buga wasa a tsakaninsu, inda Eagles din suka yi nasara sau bakwai sannan suka yi canjaras biyu.

A karo na karshe da Najeriya ta kara da Bafana Bafana a wasan neman tikitin shiga gasar cin kofin duniya shi ne kafin gasar 2010.

Eagles ta samu nasara a wasanni biyu da suka fafata, amma Afirka ta Kudu ta samu gurbin shiga gasar ba tare da la’akari da matsayin mai masaukin baki ba.

Senegal, zakarun Afirka, na rukunin na biyu ne tare da Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango da Togo da Mauritania da Sudan da kuma Sudan ta Kudu, yayin da Morroco ta samu kanta a rukuni na biyar inda za ta kara da Zambia daTanzaniada Congo Brazzaville da Niger da kuma Eritrea.

Ghana tana rukuni na daya tare da Mali, da Madagascar da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, da Comoros da kuma Chadi.

Cikakken jaddawalin

Group A: Egypt, Burkina Faso, Guinea-Bissau, Sierra Leone, Ethiopia, Djibouti

Group B: Senegal, Democratic Republic of Congo, Togo, Mauritania, Sudan and Southern Sudan

Group C: Nigeria, South Africa, Benin Republic, Zimbabwe, Rwanda and Lesotho

Group D: Cameroon, Cape Verde, Angola, Libya, Eswatini and Mauritius

Group E: Morroco, Zambia, Tanzania, Congo Brazzaville, Niger and Eritrea.

Group F: Ivory Coast, Gabon, Kenya, The Gambia, Burundi, Seychelles

Group G: Algeria, Guinea, Uganda, Mozambique, Botswana, Somalia

Group H: Tunisia, Equatorial Guinea, Namibia, Malawi, Liberia, Sao Tome e Principe

Group I: Ghana, Mali, Madagascar, the Central African Republic, Comoros and Chad.

Ranakun wasanni biyu na zagayen farkon gasar za su gudana ne a ranar 13-21 ga watan Nuwamba, 2023 sdai kuma na karshe zai kasance a ranakun 6-14 ga watan Oktoba, 2025.

Source: BBC