BBC

News

Sports

Business

Entertainment

GhanaWeb TV

Africa

Opinions

Country

Rikicin Sudan: Ana jin harbe-harbe duk da yarjejeniyar tsagaita wuta

Yan gudun hijira daga Sudan

Tue, 25 Apr 2023 Source: BBC

Da alamu yarjejeniyar tsagaita wuta Sudan tana ɗan aiki bayan an ayyana ta, da tsakar dare agogon ƙasar misalin ƙarfe 10n dare agogon GMT ranar Litinin.

Yunkuri na huɗu kenan da ake yi don tsagaita faɗan wanda aka fara ranar 15 ga watan Afrilu, sai dai a baya yarjejeniyar ba ta ɗore ba.

Sakataren wajen Amurka Antony Blinken ya ce an amince da yarjejeniyar tsagaita wuta tsawon sa'a 72 tsakanin sojojin Sudan da mayaƙa masu kayan sarki na rundunar (RSF) bayan shafe sa’a 48 ana tattaunawa.

An ba da rahoton jin amon harbe-barbe a Khartoum, babban birnin ƙasar ranar Talata.

Haka kuma an ba da rahotannin ganin shawagin jiragen yaƙi a sama, amma yanzu fararen hula sun koma gudanar da harkokinsu a titunan babban birnin.

Aƙalla mutum 459 aka kashe a rikicin ya zuwa yanzu, ko da yake ana jin cewa haƙiƙanin adadin na iya fin haka.

Duka ɓangarorin biyu da ke gwabza faɗa da juna, sun tabbatar da cewa za su sassauta.

Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, António Guterres ya yi gargadin cewa tashin hankalin na Sudan, ka iya aukar da mummunan yanayi da zai ɗaiɗaita duka yankin da ma wasu wuraren.

Tun bayan fara tashin hankalin ne aka umarci mazauna birnin Khartoum su zauna a gidajensu, abin da ya janyo ƙarancin abinci da ruwan sha.

An yi luguden bama-bamai a kan muhimman ababen more rayuwa kamar bututan samar da ruwan sha, abin da ya tilasta wa mutane shan ruwan Kogin Nilu.

Ƙasashe suna ta rige-rigen kwashe jami’an diflomasiyyansu da fararen hula a yayin da faɗan ya ƙara rincaɓewa a tsakiyar yankunan birnin mai yawan jama'a.

Akwai fatan cewa tsagaita wutar za ta bai wa fararen hula damar ficewa daga birnin.

Su ma gwamnatocin ƙasashen waje na cike da fatan hakan zai ba su damar ci gaba da kwashe mutanensu daga cikin ƙasar.

Ma’aikatar wajen Masar ta bayyana a ranar Litinin cewa an hallaka wani jam’in diflomasiyya lokacin da yake tuƙa mota zuwa ofishin jakadancinsu a birnin Khartoum don taimaka wa aikin kwashe ‘yan ƙasar ta Masar.

Jami'i mai kula da manufofin hulɗa da ƙasashen waje a Tarayyar Turai, Josep Borrell shi ma ya tabbatar a ranar Litinin cewa an kwashe ‘yan ƙasashen Turai fiye da 1,000.

Afirka ta Kudu da Kenya da kuma Uganda na cikin ƙasashen Afirka da suka sanar da kwashe mutanensu.

Gwamnatin Burtaniya ta sanar cewa za ta fara kwashe jami'anta da iyalansu na kusa daga ranar Litinin.

A ranar Litinin, Mista Blinken ya bayyana cewa ayarin wasu motoci da ke ƙoƙarin fitar da mutane sun fuskanci ‘’fashi da kwasar ganima’’.

Ya kuma ce Amurka na duba yiwuwar barin ayyukanta na diflomasiyya don ci gaba da aiki a Sudan, amma ya bayyana halin da ake ciki a can da cewa "mai cike da ƙalubale ne".

Source: BBC