BBC

News

Sports

Business

Entertainment

GhanaWeb TV

Africa

Opinions

Country

Shugaban masu rinjaye ya yi nasarar komawa Majalisar Wakilai

Nigerian Flag 3.png Tutar Najeriya

Mon, 17 Apr 2023 Source: BBC

Bayan zaɓen cike-giɓi, INEC ta bayyana Alhassan Ado Doguwa a matsayin ɗan takarar da ya lashe zaɓen ɗan majalisar wakilai daga mazaɓar Doguwa da Tudun Wada.

Karo na biyar kenan, da ɗan majalisar na tarayya ke samun nasarar zuwa majalisar wakilai daga Kano tun bayan komawar Najeriya mulkin dimokuraɗiyya a 1999.

An soke nasarar da ya samu tun farko, bayan zaɓen 25 ga watan Fabarairu, saboda jami'in sanar da sakamakon, Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai ya ce "tursasa masa" aka yi.

Ya dai ce sai an sake kaɗa ƙuri'a a tasoshin zaɓe 13.

Sai dai, jami'in sanar da sakamako a zaɓen cike-giɓi na mazaɓar, Farfesa Sani Ibrahim a ranar 15 ga watan Afrilu, ya ayyana Alhassan Doguwa a matsayin wanda ya yi nasara bayan wannan zaɓe.

Alhassan Ado Doguwa, wanda shi ne shugaban masu rinjaye a majalisar wakilai ya yi nasara ne bayan ya samu ƙuri'a 41,573, inda babban abokin fafatawarsa, Yusha'u Salisu na NNPP ya samu ƙuri'a 34,831.

Zaɓen dai, yana ɗaya daga cikin masu cike da taƙaddama a 2023, saboda tashin hankalin da aka samu a wancan karo, rikicin da ya yi sanadin ƙone-ƙone da halakar mutane.

Yana ɗaya daga cikin zaɓukan 'yan majalisar wakilai da na jihohi har guda 16 da aka ƙarasa ranar Asabar a cikin jihar Kano.

Source: BBC