BBC

News

Sports

Business

Entertainment

GhanaWeb TV

Africa

Opinions

Country

Super Eagles ta yi tuntuɓe a wasanta da Lesotho

64924684 Yan wasan Najeriya

Thu, 16 Nov 2023 Source: BBC

Najeriya ta fara wasannin neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya na 2026 da tuntuɓe inda ta yi kunnen doki da Lesotho 1-1.

A minti na 56 ne Lesotho ta fara jefa ƙwallo a ragar Super Eagles a wasansu na rukunin C a filin wasan Godswill Akpabio da ke Uyo, jihar Akwa Ibom ranar Alhamis.

Amma mintuna 11 bayan haka, mai tsaron baya Semi Ajayi ya farkewa Najeriya.

A ranar Lahadi ne Super Eagles za ta kara da Zimbabwe a filin wasa na Huye da ke Butare, a wasan da ya zame wa Najeriya dole ta yi nasara idan har tana son kara haskaka damarta ta samun gurbin shiga gasar cin kofin duniya na 2026.

Source: BBC