BBC

News

Sports

Business

Entertainment

GhanaWeb TV

Africa

Opinions

Country

Yayin da ƙasashe ke rige-rigen kwashe mutanensu, wanne hali 'yan Sudan ke ciki?

Mutane sun yi amfani da damar tsagaita wuta a yakin sun bar gidajensu

Thu, 4 May 2023 Source: BBC

Ɓangarori biyu masu fafatawa da juna na dakarun tsaro a Sudan sun amince da sabunta yarjejeniyar tsagaita wuta tsawon kwana uku, jim kaɗan kafin wadda aka ƙulla ta kawo ƙarshe.

Ƙarin sa’a 72 – ya zo ne bayan yunƙurin diflomasiyya na ƙasashe makwabta da kuma Amurka, da Burtaniya a Majalisar Ɗinkin Duniya.

Amma ana ci gaba da ba da rahotannin gwabza ƙazamin faɗa a Khartoum babban birnin ƙasar.

Yarjejeniyar da aka ƙulla a baya, ta bai wa dubban mutane damar tserewa zuwa tudun-mun-tsira, a yayin da gomman ƙasashe suka yunƙura wajen kwashe mutanensu.

Faɗan wanda aka shafe kusan mako biyu ana gwabzawa tsakanin sojojin Sudan da mayaƙan rundunar jami'ai masu kayan sarki ta RSF ya haddasa mutuwar ɗaruruwan mutane.

An sa rai, tsagaita wutar za ta kawo ƙarshe ne da misalin ƙarfe goma na safiyar Alhamis agogon GMT.

A yammacin Alhamis ne kuma, rundunar sojin Sudan ta amince da tsawaita lokacin tsagaita wutar, inda daga bisani ɗaya ɓangaren na ƙungiyar mayaƙan RSF su ma suka bi sahu.

Sudan ta Kudu ta yi tayin shirya zaman tattaunawa a ƙasarta, kuma rundunar sojin ta amince da aikewa da wakilai don hawa teburin tattaunawar.

Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya ce Washington ‘’ta yi aiki tuƙuru’’ don ganin an ƙara kwanakin tsagaita wutar, sannan ta yi nasara ganin an sassauta tashin hankalin.

Amma kuma daga bisani ne mai magana da yawun fadar White House Karine Jean-Pierre ta bayyana cewa halin da ake ciki faɗa na iya ƙara muni a kowanne lokaci.

Wanne hali mutanen Sudan ke ciki

A halin yanzu, rundunar RSF da shaidu sun ce sojoji na ta luguden wuta a sansanonisu na birnin Khartoum.

Ministar harkokin waje a tsohuwar gwamnatin farar hula, Maryam al-Sadiq al-Mahdi, ta shaida wa BBC daga gidanta a birnin Khartoum cewa duk da tsagaita wutar, fararen hula na cikin zullumi.

"Abin da suka kira yarjejeniyar tsagaita wuta, ba ta da wata alaƙa da abubuwan da ke faruwa," ta ce. "Luguden wutar da jiragen yaƙi ke yi na faruwa kusan ba dare ba rana.’’

An kuma ba da rahoton ɓarkewar faɗa a gabashin yankin Darfur da sauran larduna.

Aƙalla mutum 512 ne aka halaka a fadan, sannan wasu 4,200 ne suka jikkata, ko da yake, yawan adadin waɗanda suka mutu na iya ƙaruwa matuƙa.

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce tana tsammanin za a iya samun ƙarin mace-mace saboda ɓarkewar cutuka dalilin rashin harkokin kula da lafiya.

Jami’an lafiya sun ce akasarin asibitoci a yankunan da ake tashin hankalin ba sa aiki, sannan fiye da kashi 60 na asibitoci a birnin Khartoum ba sa aiki.

Source: BBC