BBC

News

Sports

Business

Entertainment

GhanaWeb TV

Africa

Opinions

Country

Sojoji sun kubutar da mutum 10 da aka sace a Kaduna

 117615580 Fcfc9add B60d 419c B0df 9e22eaf47136 Ranar Laraba ne sojojin na Najeriya suka ceto mutane 10.

Thu, 18 Mar 2021 Source: BBC

Gwamnatin jihar Kaduna ta tabbatar da kubutar da mutane 10 da aka sace kusan makwanni biyu da suka gabata a gidajen ma'aikatan Hukumar Kula da Filin Jirgin Sama ta Tarayya (FAAN) da ke karamar Hukumar Ikara.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida a jihar, Samuel Aruwan, ya ce a ranar Laraba ne sojojin na Najeriya suka ceto mutane 10.

Mista Aruwan, wanda ya yi wa yan jarida bayani game da ci gaban da aka samu a fannin tsaro na jihar, ya ce ba za a iya bayar da cikakken bayani game da wurin da aka kubatar da mutanen ba saboda dalilan tsaro.

A ranar juma'ar da ta gabata ne yan bindiga suka kai hari bayan da suka fasa katangar rukunin gidajen inda suka awon gaba da mutun 10 .

Bayan wannan hari ne yan bindigar suka shiga cikin kwalejin gandun daji da ke kusa da Mando inda suka yi awon gaba da mutum sama da talatin.

Source: BBC