BBC

News

Sports

Business

Entertainment

GhanaWeb TV

Africa

Opinions

Country

Ƙungiyar ISWAP ta kashe sojojin Najeriya 15

 117569595 Soldierse.png Dakarun gwamnati 13 da suka haɗa da soja 10 ne aka jikkata a harin

Sun, 14 Mar 2021 Source: BBC

Mayaƙan da ke biyayya ga ƙungiyar IS sun yi wa tawagar motocin sojan Najeriya kwanto-ɓauna a Jihar Borno, inda suka kashe mutum 19, ciki har da mayaƙan sa-kai.

Maharan na ƙungiyar Islamic State West Africa Province (ISWAP) sun far wa motocin dakarun ne a kusa da garin Gudumbali da ke yankin tafkin Chadi ranar Alhamis.

Wani jami'an rundunar sojan Najeriya da bai yarda a faɗi sunansa ba ya faɗa wa kamfanin labarai na AFP cewa "mun rasa sojoji guda 15 da kuma mayaƙan sa-kai huɗu a kwanton-ɓaunar da 'yan ta'addan suka yi mana a kusa da Gudumbali".

Ya ƙara da cewa dakarun gwamnati 13 da suka haɗa da soja 10 ne aka jikkata a harin.

Rukunin motocin guda 10 na kan hanyarsu ce ta zuwa Gudumbali daga Kukawa, duka a Jihar Borno, domin ƙaddamar da hari kan 'yan bindigar a lokacin da aka buɗe musu wuta, a cewar wani jami'in sojan.

Ranar Asabar ne Babban Hafsan Sojan Najeriya Lucky Irabor ya isa birnin Maiduguri domin tantance yadda yaƙi da Boko Haram ke gudana a karo na biyu cikin wata shida.

Har wa yau, a Asabar ɗin ne kuma ISWAP ta fitar da wata sanarwa tana iƙirarin kai harin.

Wannan hari shi ne na baya-bayan nan a yaƙin da ya yi sanadiyyar kashe mutum 36,000 kuma ya raba dubban ɗaruruwa da muhallansu a yankin arewa maso gabashin Najeriya cikin shekara 11 da suka wuce.

ISWAP wadda ta ɓalle daga Boko Haram a 2016, na yawan kai hare-hare a Najeriya, abin da ke jawo asarar rayukan sojoji da na fararen hula.

Source: BBC