Hukumar shirya jarrabawar kammala Sakandire ta Afirka ta Yamma, WEAC, ta ce ta rike sakamakon jarrabawar dalibai fiye da 260 kan zargin satar jararabawa.
To sai dai hukumar ta tanadi wani wuri na musamman a shafinta na intanet da dalibai za su iya shigar da korafinsu kan rike musu jarrabawar ga hukumar.
Haka kuma shi ma dalibin da yake ganin an rage masa maki a jarrabawar, zai iya shigar da nasa korafin domin hukumar ta gudanar da bincike.
Da zarar dalibi ya shigar da korafin hukumar za ta gudanar da bincike domin sanar da shi ainihin abin da ya sa ta rike masa jarrabawar.
A wannan bidiyon, mun kawo muku matakan da za ku bi domin gano hakikanin abin da ya sa hukumar ta rike muku sakamakon jarrabawar.
- Beware of fraudulent admission syndicate - KNUST warns
- Tertiary students raise concerns over challenges of no academic fee for level 100 policy
- Acquire skills in addition to academic qualifications - Young graduates advised
- 34 Prisoners sit for 2024 BECE
- Some free SHS beneficiaries are performing poorly in our universities - ATAG
- Read all related articles